Labarai
‘Yan kasashen waje 840,000 ne wa’adin bizarsu ya kare a Nijeriya – Gwamnati

Ministan harkokin cikin gida na Nijeriya Olubunmi Tunji Ojo ya ce ‘yan kasashen waje sama da 840,000 ne wa’adin bizarsu ya kare a kasar, kuma ba su dauki matakin sabunta ta kk ficewa ba.
Ministan ya bayyana haka ne yayin wata hira da gidan talabijin na Channels, inda ya ce mutanen sun kasance ‘yan kasashen duniya daban-daban.
Wannan ya zo a daidai lokacin da ake ta cece-kuce kan wata yarjejeniya da Nijeriya ta kulla da kasar Birtaniya kan hadin gwiwa a fannin shige da fice, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Sai dai ministan ya jaddada cewa, Nijeriya ba za ta amince da karbar daurarru ko masu laifi daga wata kasa ba, sannan babu batun bayar da mafaka ga masu gudun hijira daga ketare.
You must be logged in to post a comment Login