Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Ya kamata Bola Tinubu yayi taka tsan-tsan wajen yankewa Nijar hukunci- Gamayyar ƙwararru ta Nijeriya

Published

on

Gamayyar ƙwararrun a Nijeriya ta yi kira ga Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi taka-tsantsan wajen ɗaukar matakan mayar da jamhuriyar Nijar kan turbar dimokraɗiyya, bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa shugaba Mohamed Bazoum.

A wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da gamayyar ta aika wa Shugaba Tinubu, ta ce akwai buƙatar kasar nan ta zamo mai sara tana duban bakin gatari game da matsayarta a kan abin da ke faruwa a Nijar, musamman bisa la’akari da daɗaɗɗiyar dangantaka mai kyau tsakanin ƙasashen biyu, aminan juna.

Shugaban kasa, Bola Tinubu, shi ne ke jagorantar Ƙungiyar Raya Ƙasashen Afirka ta Yamma wato Ecowas da ta bai wa sojoji masu mulki a Nijar wa’adin kwana bakwai, don su mayar da mulki hannun hamɓararren shugaban ƙasa Bazoum Mohamed ko kuma ta ɗauki matakin amfani da ƙarfi a kansu.

Gamayyar wadda ta ƙunshi ƙwararru daga ɓangarori daban-daban na rayuwa, ta bi sahun Ecowas da sauran ƙasashen da ƙungiyoyin duniya wajen yin Allah-wadai da juyin mulkin na Nijar, amma ta ce hanyar lumana ta fi dacewa a bi wajen warware matsalar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!