Labarai
Yan sanda sun tarwatsa masu garkuwa da mutane a titin Funtua zuwa Gusau

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce, ta dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a kan titin Funtua zuwa Gusau a jihar Katsina.
Mai magana da yawun rundunar na kasa ACP Muyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar.
sanarwar ta ruwaito cew, jami’an rundunar sun yi nasarar dakile yunkurin sace wasu mutane goma da kuma direbobi biyu da fasinjoji takwas ba tare da an samu wadanda suka ji rauni ba.
Haka kuma, rundunar ta ce, jami’an nata sun yi artabu da ‘yan bindigar wadanda ke dauke da muggan makamai, lamarin da ya tilasta wa bata garin tserewa da raunukan harbin bindiga.
You must be logged in to post a comment Login