Connect with us

Labarai

Yan sandan Plateau sun tabbatar da mutuwar mutane 3 a harin da yan bindiga a Pwomol

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Plateau, ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan wani hari da ‘yan bindiga suka kai a ƙauyen Pwomol da ke ƙaramar hukumar Barkin Ladi da safiyar ranar Litinin.

 

Wadanda aka kashe din sun hada da matasa biyu da wani dattijo, yayin da wani mutum guda kuma ya jikkata.

 

Mai magana da yawun rundunar, Alabo Alfred, ya ce, jami’an tsaro sun kai ɗauki cikin gaggawa tare da fafatawa da maharan, lamarin da ya sa suka tsere zuwa dazuka.

 

Ya ƙara da cewa an kama wani da ake zargi, wanda yanzu haka ya ke tsare yayin da ake ci gaba da bincike domin cafke sauran.

 

A nasa ɓangaren, Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Bassey Ewah, ya jajanta wa iyalan mamatan tare da shan alwashin cewa za a tabbatar da adalci kan lamarin.

 

Haka kuma, ɗan majalisar yankin, Dickson Y. Chollom, ya yi Allah-wadai da harin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!