Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yanzu-yanzu: Ƴan bindiga sun sako attajirin da suka sace a Kano

Published

on

Rohotonni da ke fitowa yanzu-yanzu daga garin Minjibir na cewa ƴan bindiga sun sako attajirin nan Alhaji Abdullahi Bello Kalos da aka sace a garin Minjibir da ke nan Kano.

Wani makusancin attajirin ya shaida wa Freedom Radio cewa, Alhaji Abdullahi Kalos ya dawo da misalin ƙarfe 4 na asubahin yau Asabar, bayan ya shafe kwanaki uku a hannunsu.

‘Yan uwan Alhaji Abdullahi Kalos ne suka karbo shi a wani kauye da ke karamar hukumar Babura ta jihar Jigawa.

Jami’in hulda da ‘yan sandan Kano DSP. Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da faruwar lamarin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!