Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yanzu-yanzu: An ceto matashin da ya rataye kansa a Kano

Published

on

Rahotanni daga unguwar Ƴan Kaba da ke nan Kano na cewa an samu wani matashi ya rataye kansa a jikin bishiya

Matashin ɗan shekaru 29 mai suna Mukhtar Umar ya rataye kan nasa ne a daren ranar Asabar.

Daga bisani ne kuma al’umma suka farga, suka sanar da jami’an tsaro, inda baturen ƴan sanda na Bompai SP. Aliyu Musa ya jagoranci ƴan sanda domin ceto shi.

Jami’in hulɗa da jama’a na ƴan sandan Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya shaida wa Freedom Radio cewa, ƴan sanda sun ceto matashin cikin ƙoshin lafiya.

Sai dai a cewar sa, ƴan uwan matashin sun shaida musu cewa ya taɓa samun larurar ƙwaƙwalwa saboda ta’ammali da miyagun ƙwayoyi.

DSP. Kiyawa ya ce, yanzu haka sun shiga faɗaɗa bincike kan matashin domin ɗaukar matakin da ya dace.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!