Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yawan ambaliyar ruwa ke haddasa karancin abinci – Masani

Published

on

Wani masanin harkokin Noma anan Kano ya alakanta matsalar karancin abinci da yawan samun ambaliyar ruwa a gonaki da ake yi.

Masanin harkokin Noman ya kuma alakanta rashin hadin kan manoma da cewa na daya daga abinda ke kawo koma baya ta bangaren bunkasar noma.

Dakta Munir Muhammad Yawale ne ya bayyana hakan a yayin zantawarsa da wakiliyarmu Safara’u Tijjani Adam a wani bangare na bikin ranar abinci ta duniya da ake gudanarwa a yau.

Dakta Munir ya ce kamata yayi manoma su rika lura da yanayin gonar su kafin su yi shuka domin kiyaye abkuwar ambaliyar ruwan.

Majalisar dinkin duniya ce dai ta ware ranar 16 ga watan oktobar kowacce shekara a matsayin ranar abinci ta duniya, sai a biyo mu nan bada kadan don jin cikakken rahoton.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!