Connect with us

Labarai

Yawancin waɗanda suka soke ni a baya sun koma APC- Wike

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Rivers, kuma ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana cewa yawancin waɗanda suka soke shi a baya, yanzu sun koma jam’iyyar APC, jam’iyyar da shi ma yake cikinta a halin yanzu.

Wike ya bayyana hakan ne yayin wata hira da manema labarai a Abuja, inda ya ce lokaci ne ya tabbatar da cewa siyasar sa ta gaskiya ce ba ta son zuciya ba.

Ya ce, mutanen da suka zarge shi da cin amanar jam’iyyar PDP yanzu su ne suka rungumi APC da hannunsu biyu-biyu.

Ministan ya kuma jaddada cewa siyasa ta na buƙatar fahimta da aiki don ci gaban kasa, ba wai yin suka kawai saboda banbancin jam’iyya ba.

A cewarsa, Lokacin ya nuna waye mai gaskiya da kuma wanda yake wasa da hankalin jama’a.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!