Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yemi Osinbajo ya bayyana Imam Abdullahi Abubakar, a matsayin gwarzo abun koyi

Published

on

Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana malamin addinin Islaman nan da ke jihar Filato wanda ya ceci rayukan wasu mabiya addinin kirista da ‘yan bindiga suka biyo, Imam Abdullahi Abubakar, a matsayin gwarzo kuma abun koyi.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai Magana da yawun shugaban kasa Laolu Akande.

Sanarwar ta ce Osinbajo ya bayyana hakan ne lokacin da ya karbi bakuncin Limamin wanda ya kai ziyara fadar shugaban kasa a jiya Alhamis.

A ranar 23 ga watan Yunin bara ne Imam Abdullahi Abubakar limamin masallacin kauyen Yelwan Gindin Akwati a yankin karamar Hukumar Barikin Ladi a jihar Filato ya boye mutanen a masallacin sa bayan da ‘yan bindiga suka biyo su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!