Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar shige da fice ta ja kunnen wasu jami’anta kan cin hanci

Published

on

Kwanturola Janar na hukumar kula da shige da fice ta Najeriya Muhammad Babandede, ya shawarci manyan jami’an hukumar hamsin da uku wadanda aka yiwa karin girma da su guji cin hanci da rashawa, kuma su guji son zuciya yayin gudanar da ayyukansu.

Muhammad Babandede ya bayyana hakan ne yayin bikin karin girma ga jami’an wanda ya gudana a shalkwatar hukumar da ke Abuja.

A cewar kwanturola Janar na hukumar kula da shige da fice ta Najeriya, kwarewa da kuma jajircewar su a aiki shiyasa aka ga dacewar yi musu karin girma, a don haka ya hore su da su zage dantse wajen ganin sun kare mutuncin kasar nan.

Rahotanni sun ce mataimakan kwanturolan jihohi guda hamsin da uku ne aka yiwa karin girma zuwa mukamin kwanturola.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!