Connect with us

Labarai

Yobe: Mutum 1 ya rasu 16 kuma sun jikkata a hatsarin mota

Published

on

Mutum ɗaya ya rasu, yayin da wasu mutane goma sha shida suka jikkata sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya auku a karamar hukumar Karasuwa, ta jihar Yobe.

 

Shaidu sun bayyana cewa hatsarin ya faru ne sakamakon irin tseren ganganci da direban motar ya yi, lamarin da ya jawo ta kauce daga hanya.

 

Hukumar kiyaye haddura ta ƙasa, ta tabbatar da faruwar hatsarin, inda ta ce tuni aka garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibiti domin samun kulawar gaggawa.

 

Hukumar ta kuma yi kira ga direbobi da su rika bin ƙa’idojin hanya, domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!