Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Da ɗumi-ɗumi: Gwamnatin tarayya ta shawo kan matsalar lantarki

Published

on

Ma’aikatar lantarki ta ƙasa ta ce ta shawo kan matsalar rashin wutar da aka fuskanta a farkon makon nan.

Ministan Lantarki Injiniya Abubakar D. Aliyu ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar yau Asabar.

Sanarwar ta ce, an samu matsalar katsewar lantarkin ne sakamakon ƙarancin Gas da kuma ayyukan masu fasa bututun da ke samar da wutar lantarki.

Ministan ya ce, yanzu haka an gyara bututun Gas ɗin tashar lantarki ta Okpai da ke jihar Delta wadda wasu ɓatagari suka lalata.

Ta cikin sanarwar ministan ya yiwa ƴan Najeriya albishir da cewa, ana daf da kammala gyaran ƙarin tashoshin lantarki da aka dakatar da aikinsu saboda gyara daga lokaci zuwa lokaci.

Daga ƙarshe ministan lantarkin ya ce, Gwamnati na ci gaba da ɗaukar matakai ganin cewa ba a sake samun irin wannan matsalar ba a nan gaba.

Labarai masu alaƙa:

Buhari ya amince da kwangiloli 16 domin bunƙasa wutar lantarki

Za’a daga matsayin tashar wutar lantarki ta jihar Yobe

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!