Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za’a daga matsayin tashar wutar lantarki ta jihar Yobe

Published

on

Gwamnatin tarayya zata daukaka matsayin tashar yada wutar lantarki ta jihar Yobe domin fadada ta yadda zata iya samar da karin wutar lantarki da zata wadaci al’ummar jihar Yobe.

Ministan lantarki Injiniya Abubakar D. Aliyu ne ya bayyana hakan yau labara yayin ziyarar gani da ido a babbar tashar wutar lantarki ta jihar Yobe dake babban birnin jihar Damaturu.

Ministan wanda shugaban kamfanin raba wutar lantarki na kasa wato TCN Injiniya Sule Abdulazeez ya wakilta, ya kuma ce karuwar bukatar wutar lantarki a yankin ya nuna tashar wutar lantarki tana bukatar a daga matsayinta.

“An bada kwangilar samar da naurar da zata kara yawan wutar lantar mai karfin Volt-Amps (MVA) miliyan 150 a tashar wutar lantarkin ta jihar Yobe,” inji ministan.

Injiniya Abubakar D. Aliyu ya yabawa hukumomin tsaro saboda kokarinsu wajen samar da tsaro ga tashar wutar lantarki

Minis yayi kira ga jama’ar dake kusa da tashar wutar lantarkin su kula da ita domin ta ci gaba da amfanar al’umma baki daya.

A watan Fabrairu na 2019 ne shugaba Muhammadu Buhari ya kaddamar da babbar tashar wutar lantarkin da take Damaturu babban birnin jihar Yobe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!