Connect with us

Labarai

Za a fuskanci ruwan sama da iska mai karfi a Arewacin Najeriya- NiMet

Published

on

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya NiMet, ta yi hasashen cewa, daga yau Litinin zuwa Laraba za a fuskanci ruwan sama da iska mai karfi  a sassa daban-daban na Arewacin Najeriya.

 

Ta cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar da yammacin Lahadi, ta ce. jihohin da za su fuskanci yanayin sun hada da  Kebbi da Zamfara da Sokoto sai Gombe da Borno da kuma Yobe.

 

Haka kuma, a cewar rahoton, za a samu mamakon ruwan sama da tsawa a jihohin Bauchi da Yobe da Jigawa sai Kano da Kaduna da Zamfara da Katsina da Adamawa sai Taraba da kuma Borno.

 

Hukumar ta shawarci manoma da matafiya a yankunan  da abun ya shafa da su kasance cikin shiri domin guje wa hadurran da ka iya biyo bayan ruwan sama mai karfi da kuma iska.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!