Connect with us

Ƙetare

Za mu buɗe mashigar Hormuz ko ta halin ƙaƙa – Trump

Published

on

Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce ”nan ba da jimawa ba za mu buɗe mashigar Hormuz ko ta halin ƙaƙa”, don jirage su wuce cikin kwanciyar hankali.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Mista Trump ya ce yana fatan China da Faransa da Japan da Koriya da Kudu da kuma Birtaniya za su aika jiragen ruwa na yaƙi zuwa mashigar ”domin kare duk wata barazana” daga Iran.

Ya ƙara da cewa ƙasasashe da dama za su aika jiragen ruwansu na yaƙi domin tabbatar da ”tsaro a mashigar”

Ya ce a yanzu Amurka za ta ci gaba da kai hare-haren bama-bamai kan jiragen ruwan Iran da ke wajen mashigar”.

Ya yi iƙirarin cewa Amurka ta ”lalata kashi 100 na ƙarfin sojin Iran, amma ya ce takan yi amfani da jirage marasa matuƙa da dasa nakiyoyi da kuma makamai masu linzami masu cin gajeren zango.

Wakilin Iran a Geneva, Ali Bahrani ya ce iƙirarin Trump ɗin na lalata ƙarfin sojin Iran ”ƙirƙirarren labari ne”.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!