Connect with us

Labarai

Za mu ci gaba da bayar da tallafi a fannin tsaro- Mazauna Danbare

Published

on

Kungiyar ci gaban unguwar Gangar Ruwa Tudun Tsakuwa da ke yankin Dan Bare a karamar hukumar Kumbotso ta sha alwashin ci gaba da tallafawa musamman ma a harkokin tsaro don dakile aikata laifuka.

Shugaban kungiyar Nura Abdullahi Azara, ne ya bayyana hakan yau lahadi lokacin da suke mika ofishin da suka samar ga rundunar tsaro ta Civil Defence don inganta tsaro a yankin.

Ya ce, yawan iyakokin unguwar da ke kawo musu barazanar tsaro na cikin dalilan da suka sanya su samar da ofishin.

A nasa jawabin shugaban karamar hukumar Kumbotso Abdullahi Gali Basab, cewa ƴa yi yunkurin da mazauna Yankin suka yi abu ne da ya kamata sauran unguwanni su yi koyi da shi don inganta harkokin tsaro.

A nasa jawabin, kwaamandan Rundunar tsaro ta Civil Defence na Kano Shafiu Abdulmuminu, wanda mataimakin sa Ishaq Ibrahim Abdullahi, ya wakilce shi ya ce, za su tabbatar da tsarin aikin jami’an na tabbatar da bin doka ba tare da cin zarafi ko shiga aikin da ba nasu ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!