Connect with us

Labarai

Za mu  daina tura shanu  zuwa jihohin Kudu- Gwamna Bago

Published

on

Gwamnatin  jihar Neja ta ce, za ta  daina tura shanu  zuwa wasu jihohin Kudu nan gaba kadan a wani mataki na bunkasa harkokin fannin Noma da Kiwo.

Gwamnan Jihar Nijar Umar Bago, ne ya bayyana hakan  yayin da ya ke yin karin haske a wajen wani taron tattalin arziki da bunkasa fannin noma da ya gudana a baya baya nan a jihar Lagos.

Bago ya sanar da cewa jihar sa za ta daina kai shanu kai tsaye zuwa kasuwannin Lagos da Ogun da wasu jihohin Kudu.

A cewar gwamna Umaru Bago, hakan zai ba manoma da makiyaya damar cin moriyar amfanin da suka yi.

Haka kuma, gwamnan ya ce, jihar ta Neja za ta kara yawan filayen gona da ta ware wa jihar Lagos daga kadada 20,000 zuwa 100,000 domin kara inganta hadin kai wajen samar da abinci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!