Connect with us

ilimi

Za mu dauki nauyin karatun duk mahaddacin da ke shirin yin karatun Boko- Gwamna Radda

Published

on

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya ce, gwamnatinsa za ta ɗauki nauyin karatun duk wanda ya haddace Alƙur’ani kuma ya ke son ci gaba da ilimi a fannonin zamani kamar likitanci ko unguwanzoma da sauran fannonin ayyukan zamani.

Gwamnan ya bayyana haka ne a babban taron da aka gudanar domin gyara tsarin karatun Almajiri da Islamiyya a jihar, inda malamai, shugabannin al’umma, ƙungiyoyi da hukumomi suka halarta.

Radda ya ce, gwamnati za ta kafa sabbin makarantu guda uku da za su haɗa mahaddata Alƙur’ani da ilimin zamani irin su Turanci, Lissafi da koyon sana’o’in hannu ga yara maza da mata.

Ya kuma jaddada cewa malamai za su taka muhimmiyar rawa wajen jagorantar wannan shirin, in da ya bukaci   iyaye da al’umma da su bayar da goyon baya domin gwamnati kaɗai ba za ta iya magance matsalar almajiranci ba.

Rahotonni sun nuna cewa sama da yara 300,000 ne ba sa zuwa makaranta a Katsina, ciki har da dubban almajirai da ‘yan mata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!