Connect with us

Labarai

Za mu fara hukunta iyayen da ba sa kai yara makaranta- Gwamnatin Gombe

Published

on

Gwamnatin Jihar Gombe ta ce za ta soma hukunta iyaye da masu kula da yara da ba sa tura su zuwa makaranta, bisa tanadin dokar SUBEB ta shekarar 2021.

Shugaban Hukumar Ilimin Bai-ɗaya ta jihar, Babaji Babadidi, ne ya bayyana haka a yayin ƙaddamar da gangamin shiga makaranta na shekarar 2025 zuwa 2026 a Amada da ke ƙaramar hukumar Akko a ranar Litinin.

Ya ce dokar ta tanadi hukuncin tara ko zaman gidan Yari na wata ɗaya ga iyayen da suka saɓa, sannan sake aikata hakan na iya kai wa ga zaman gidan yari har na tsawon watanni biyu.

Kwamishinar Ilimi ta jihar, Farfesa Aishatu Maigari, ta bayyana cewa fiye da yara 700,000 ne ba sa zuwa makaranta a Gombe, tana mai jaddada cewa gwamnati na kashe kuɗaɗe sosai a bangaren ilimi, don haka lokaci ya yi da iyaye za su dauki nauyin tura ’ya’yansu makaranta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!