Connect with us

Labarai

Za mu fara shirin sauya wa tubabbun yan bidiga tunani- Gwamnatin Katsina

Published

on

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana cewa za ta fara wani sabon shiri na koyar da tsoffin ƴan bindiga da suka miƙa wuya, domin sauya musu tunani da kuma koyar da su sana’o’in dogaro da kai.

 

Shirin, wanda hukumar ilimin manya ta jihar ke jagoranta, zai haɗa da buɗe ajujuwa na karatun boko da na addini, da kuma darussa na faɗakarwa kan illolin kashe mutane da neman fansa.

 

Daraktar hukumar ilimin manya ta jihar, Bilkisu Muhammad Kakai, ta shaida wa manema cewa nan ba da jimawa ba za a fara aikawa da malamai zuwa ƙananan hukumomi domin koyar da waɗanda suka tuba.

 

A cewar jami’ar , an kirkiri shirin ne da nufin gyara tunanin  matasan da suka shiga harkar ta’addanci, tare da tallafa musu su koma cikin al’umma  da rayuwa mai kyau.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!