Connect with us

Labarai

Za mu haɗa kai da kamfanoni don samar da filaye da gidaje- Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ya ce gwaamnatinsa za ta hada kai da kamfanonin da ke samar da filaye da gidaje don saukaka hanyoyin da ma’aikatan gwamnati da kuma sauran mutane masu karamin ƙarfi za su mallaki muhalli cikin sauki.

Gwamna Abba Kabir Yusif, wanda kwamishinan ma’aikatar gidaje na jihar Ibrahim Adamu Yakubu, ya wakilta yayin bude ofishin kamfanin Mshel Homes.

A nata jawabin, shugabar kamfanin a nan Kano Jamima Boro, cewa ta yi kamfanin yazo Kano ne don sauƙaƙa wa al’umma hanyoyin malakar filaye da gidaje.

Taron bude kamfanin ya samu halartar hukumomin Gwamnati da yan kasuwa da sauran masu ruwa da tsaki a harkokin kasa da muhalli.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!