Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Babu gudu ba ja da baya kan gyara gidaje da filaye mallakin gwamnati – Ganduje

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tace, babu gudu ba ja da baya akan yunkurinta na gyara duk wasu gidaje ko filaye mallakin gwamnati wadanda ba’a amfani dasu a ko ina suke domin sake ingantasu ta yadda zasu rika samarwa da gwamnati kudaden shiga.

Kwamishinan sharia kuma Atoni janar na Kano Barista Lawan Abdullahi Musa ne ya bayyana hakan a yau a ya yin zantawarsa da manema labarai.

Lawan Abdullahi ya kara da cewa, ya yi mamaki yadda kungiyar ma’aikatan kotu suka gurfanar da gwamnati a gaban babbar kotun Kano kasancewar suna da masaniya kan yadda tsarin shigar da kara wadda ta shafi al’amuran albashin ma’aikata yake da shi, amma suka gurfan ar da gwamati a gaban kotun.

Haka kuma kwamishinan yace kotun da’ar ma’aikata ce kadai keda hurumin sauraron karar da kungiyar ma’aikatan Kotuna suka shigar a babbar kotun jiha kan batun zabtare musu albashi da gwamnati ta yi amma gwamnatin zata yi biyayya da hukuncin Kotun.

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Tukuntawa ya rawaito cewa Barista Lawan Abdullahi na cewa gwamnatin Kano ta sauyawa kamfanin buga jarida na TRIUMPH guri zuwa rukunin gidaje na SheIkh Isyaka Rabiu domin cigaba da gudanar da ayyukansu a can.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!