Connect with us

Ƙetare

Za mu taimaka wa Najeriya wajen yaki da rashin tsaro a Arewacin kasar – Emmanuel Macron

Published

on

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce ƙasarsa za ta taimaka wa Najeriya domin shawo kan matsalar tsaro da ke addabar arewacin ƙasar.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na dandalin X, shugaba Macron ya ce ya nemi sauran ƙasashe ƙawayensu da su “ƙara ƙaimi a hulɗarsu” da Najeriya.

“Na yi magana da Shugaban Najeriya Bola Tinubu, na shaida masa goyon bayan Faransa game da matsalolin tsaro musamman a arewacin Najeriya,” a cewar Macron.

Kalaman Macron na zuwa ne yayin da Shugaban Amurka Donald Trump ke zargin gwamnatin Najeriya da ƙyale ‘yanbindiga suna yi wa mabiya addinin Kirista kisan gilla, iƙirarin da gwamnatin Tinubu ta musanta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!