Connect with us

Labarai

Za mu yi haɗin gwiwa da Gwamnatin Kano don bunƙasa kirkire-kirkire da makamashi- Gwamnatin tarayya

Published

on

Ministan Kirkire-Kirkire da Kimiyya da Fasaha Uche Nnaji, ya bayyana cewa ma’aikatarsa za ta yi haɗin gwiwa da Gwamnatin jihar Kano domin bunƙasa kirkire-kirkire da harkokin makamashi.

 

Ministan ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da aka fitar a baya-bayan nan, inda ta bayyana ministan ya bayyana hakan ne lokacin da ya karɓi bakuncin Kwamishinan ma’aikatar Kirkire-kirkire, da Kimiyya da Fasaha na Kano Dakta Yusuf Kofar Mata, a ofishinsa da ke Abuja.

 

A cewar sanarwar, ministan ya bayyana jihar Kano a matsayin “jihar da ta fi kowacce muhimmanci a tsarin sauyin ci gaba na gwamnatin tarayya ta fuskar kirkire-kirkire.”

 

Ministan ya kuma yaba da yadda jihar Kano ke aiwatar da shirye-shiryen kirkire-kirkire kamar yadda Dakta Yusuf Kofar Mata ya sanar da shi.

 

Daga cikin waɗannan shirye-shirye akwai shirin wayar da kan matasa da masu sana’o’i a fannin fasahar zamani, da kuma sauya makarantun sakandire guda 44 zuwa cibiyoyin koyon sana’o’i da fasaha domin ƙarfafa ilimin sana’a da kasuwanci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!