Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

An samar da kwalejin kirkire-kirkire da fasaha don bunkasa fasaha – Darakta

Published

on

Kwalejin kirkira da fasaha ta jihar Kano, ta bayyana cewa an samar da ita ne da nufin kara bunkasa fasahar kirkira da zane-zane don baiwa matasa damar dogara da kan su.

Daraktan kwalejin Malam Mustapha S. Mu’azu ne ya bayyana hakan ta cikin shirin “Barka da Hantsi” na nan tashar freedom rediyo da ya mayar da hankali kan fasahar kirkira.

Malam Mustapha Mu’azu ya kara da cewa, kasancewar asalin makarantar ta al’kur’ani ce amma aka zamanantar da ita, ta yadda ake koyar da harkokin fasaha da kirkira, musamman ga matasa.

Malamin ya kuma kara dacewa shiga kwalejin ba’a bukatar wani mataki na karatu kafin shiga makarantar.

Sai dai yace kwalejin zata fara bada takardar shedar Digiri wanda hadin gwiwa ne da jami’ar karutu daga gida wato NOUN.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!