Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu zakulo matasa masu basira don basu gurbin karatu a Maryam Abacha – Dakta Bala

Published

on

Daga: Hajara Hassan Sulaiman

 

Jami’ar Maryam Abacha da ke Maradi a jamhuriyar Nijer ta ce za ta mayar da hankali wajen zakulo yaran da suke da fasaha kuma basu da damar shiga makaranta don ba su tallafin yin karatu.

 

Daraktan kulla alaka da hadin guiwar na kasa da kasa a jami’ar Maryam Abacha Dakta Bala Muhammad Tukur ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala shirin Barka da Hantsi na nan tashar Freddom Redio.

 

Dakta Bala Muhammad ya kuma ce, a yanzu jami’ar ta samar da cibiya anan Kano don saukakawa dalibai ketarawa zuwa sassa daban-daban na duniya don neman ilimi.

 

Ya ce, “wannan ya sanya a yanzu da aka samar da cibiyar makarantar anan Kano za mu binciki masu unguwanni da dagatai har ma da hakimai da amsu unguwanni don su bamu rahoton yaron da yake da basira don mu bashi gurbin karatu a jami’ar”

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!