Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu zamanantar da tashoshin mota – Muhammad Dig

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce, ta fara shirin gina sabbin wuraren ajiye motoci domin zamanantar da harkar sufuri a jihar.

Mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin sufuri Alhaji Dalladi Idris Karfi ne ya bayyana hakan a madadin kwamishinan ma’aikatar sufuri Alhaji Mohammad Ibrahim Diggol a ziyarar da ya kai tashar Mota da ke Unguwa Uku.

Alhaji Dalladi Idris Karfi ya ce, an shirya ziyarar ne domin gano kalubale da matsalolin da ake fuskanta a bangaren sufuri.

A cewar sa, zamanantar da duk wasu tashohin moto a Kano zai bada dama wajen yin gogayya da sauran tashoshin kasashen da suka ci gaba a harkar sufuri.

Sai dai Alhaji Dalladi Idris Karfi ya bukaci ‘yan kungiyar ma’aikatan sufurin mota da su bada hadin kai wajen domin cimma burin da aka sa gaba.

Hakan na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na ma’aikatar sufuri Ibrahim Adamu Kofar Nassarawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!