Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Zamu gina Asibitoci a sabbin masarautu 4 na Kano- Ganduje

Published

on

Gwamnatin jihar Kano tace tuni ta bayarda kwangilar gina Asibitoci a dukkannin sabbin masarautin jihar Kano hudu wadanda zasuci gadaje dari hudu domin bunkasa harkar lafiya a jihar Kano.

Sakataren gwamnatin Kano Alhaji Usman Alhaji ne ya bayyana hakan a yayin taron Kungiyar Likitocin kananan yara ta kasa NAPCON.

Alhaji Usman Alhaji yace banda gwamnatin jihar Kano babu wata jiha a fadin Najeria data warewa bangaren lafiya kaso mafi yawa acikin kasafin kudinta sai jihar Kano.

Sakataren gwamnatin jihar Kano Usman Alhaji ya kuma nanata cewa gwamnatin jihar Kano zata cigaba da bunkasa harkar lafiya domin ciyarda bangaren lafiya gaba.

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim Tukuntawa ya ruwaito cewa Sakataren gwamnatin Kano Usman Alhaji na cewa gwamnatin Kano zata cigaba da baiwa bangarorin ilimi da lafiya fifiko sama da komai kamar yadda Majalisar dinkin duniya ta shaida cewa duk kasar dake son cigaba dole ne sai ta fifita wadannan bangarori guda biyu

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!