Tsaro
Zamu magance matsalar rashin tsaro a Najeriya – Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa ‘yan Najeriya da rundunar sojin kasar cewa gwamnati za ta yi nasara kan matsalolin tsaro da ke addabar kasar.
Jaridar Daily Nigerian ta ambato Tinubu ya bayyana haka ne yayin buda baki da sojoji a fadar shugaban kasa da ke Abuja, inda ya yaba wa jarumtaka da sadaukarwar da jami’an tsaro ke yi wajen kare kasar daga ‘yan ta’adda.
Ya kuma jaddada kudurin gwamnatinsa na kara zuba yin abin da ya dace wajen samar da kayan aiki, bayanan sirri da tallafin aiki domin kara inganta ayyukan rundunar.
You must be logged in to post a comment Login