Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zamu saka idanu domin ganin an tafiyar da sabuwar dokar zabe a Najeriya – CISLAC

Published

on

Ƙungiyar CISLAC mai sa ido kan ayyukan majalisun dokokin Najeriya ta ce za ta saka idanu domin ganin an tafiyar da sabuwar dokar zabe da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanyawa hannu.

A yau Juma’a 25 ga watan Fabrairun 2022 shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sanyawa dokar hannu.

Shugaban kungiyar Kwamred Auwal Musa Rabsan Jani, kuma jami’in kungiyar Transparency International mai yaƙi da cin hanci da rashawa, a Najeriya ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da Freedom Radio.

Auwal Musa Rabsan Jani ya ce “ Sanyawa dokar hannu da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi zai rage cin hannu da rashawar dake damun kasar nan”.

Ya kuma ce “ yiwa dokar zabe karan tsaye da wasu daga cikin shugabannin Najeriya ke yi zai kau daga lokacin da dokar ta fara aiki”.

Auwal Musa Rabsan Jani ya kuma godewa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan kokarin da ya yi na sanyawa dokar hannu duk kuwa da cewa wasu daga cikin ‘yan siyasar Najeriya basu so hakan ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!