Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zamu samar da wutar lantarki a yankunan karkara – Buhari

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce shirye-shirye sun yi nisa na samar da wutar lantarki a karkara wanda gidaje a kalla miliyan biyar za su amfana da kudin sa ya kai sama da Tiriliyan biyu karkashin shirin bunkasa harkokin tattalin arziki.

Karamin ministan harkokin wutar lantarki Mr Goddy Jedy-Agba ne ya bayyana hakan yayin kaddamar da wutar Lantaki mai da zata mamaye yankin karu da ke birnin tarayya Abuja.

Mr. Goddy ya ce, gwamnatin tarayya zata baiwa mazauna karkara kulawar da ta dace wajen samar musu da hasken wutar lantarki wanda hakan zai taimaka musu wajen gudanar da kananan sana’o’in dogaro da kai.

Mr Goddy ya kara da cewa, mazauna karkara sun fi mayar da hankali wajen biyan kudin wuta fiye da mazauna cikin gari, a don haka a yanzu za su samu wadatacciyar wutar lantarki don magance matsalolin su.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!