Connect with us

Labarai

Zamu zamanantar da wuraren wasanni a Kano-Ogan Boye

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta jaddada kudurinta na zamanantar wa tare da inganta wuraren wasanni a Jihar nan.

Mai ba wa Gwamna Shawara na musamman kan harkokin Matasa da Wasanni, Amb Yusuf Imam Shu’aibu Ogan Boye shine ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar Gani da Ido wuraren wasanni a jihar nan.

Ambasada Yusuf Ogan Boye ya kuma bayyana rashin jin dadinsa kan abunda ya kira da rikon sakainar kashi da yace gwamnatin da ta gabata tayi da yayi sanadiyar lalacewar kayayyaki,da kuma filayen wasannin,inda ya kuma bada tabbacin cewa gwamnati mai ci zata inganta harkokin bangaren.

Wuraren da Mai ba wa Gwamnan Shawara ya ziyar ta sun hada da Gwagwarwa, Ado Bayero square, filin wasa na Kano Filas ,da dai sauran su.

Rahoton: Yusuf Sulaiman

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!