Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Sojojin Kasar Niger sun tabbatar da juyin Mulki a kasar

Published

on

A daren jiya laraba ne dakarun sojin Jamhuriyar Nijar suka sanar da hambarar da gwamnatin Muhammad Bazoum sa’oi bayan rade-radin yiwuwar juyin Mulki.

Rundinar sojin tabakin Kakakin ta Manjo Ahmadou Abdrahamane ne ta sanar da juyin mulkin,sakamakon abunda suka kira da halin rashin tsaro Nijar din ke ciki, da kuma halin rashin tabbas da suka ce tattalin arzikin kasar ya shiga.

Haka kuma Sun sanar da rushe kundin tsarin mulkin ƙasar, hadi da kulle dukkanin iyakokin kasar.

Kawo yanzu dai Babu labarin halin da Mohamed Bazoum ke ciki.

Yanzu haka dai sojin sun sanar da dokar Hana fita daga karfe 10 dare zuwa karfe 6 na safe.

Wannan dai shine juyin mulki na huɗu da kasar Nijar din ta fuskanta tun bayan samun ‘yancin kai daga kasar Faransa a shekarar 1960, bayan yunkurin juyin mulkin da dama da ba ayi nasara ba a kasar.

Rahoton: Yusuf Sulaiman

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!