Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zan ci gaba da kare kaina a gaban kotu – Abduljabbar

Published

on

Malamin nan Abduljabbar Kabara ya bayyanawa kotu cewa zai ci gaba da kare kansa a gabanta.

Wannan dai na zuwa ne bayan da kotun ta ce lauyoyinsa sun miƙa mata takardar ficewa daga daga shari’ar.

Ko da kotu ta tambayi Abduljabbar ɗin kan ficewar lauyoyinsa daga shari’ar sai ya ce “Ina da masaniyar hakan hasalima ni ne na koresu sakamakon sun saɓa yarjejeniyar da muka ƙulla“.

Dan haka Malamin yace shi yanzu a kyaleshi zai ci gaba da kare kansa anan ne mai gabatar da ƙara ya tashi yace ai a ƙa’ida ba za’a ci gaba da shari’ar ba tare da Lauya ba.

A yau ne dai aka ci gaba da sauraran shari’ar da ake yi tsakanin gwamnatin jihar Kano da Malam Abduljabbar Kabara a babbar kotun shari’ar musulunci da ke zamanta a kofar kudu ƙarƙashin jagorancin mai Sharia Ibrahim Sarki Yola.

Inda Lauya mai gabatar da ƙara Farfesa Nasir Adamu Aliyu ya jagoranci sauran lauyoyin.

Daga ƙarshe kotum ta ce a rubuta takarda zuwa ga hukumar dake kula da lauyoyi don su bai wa Abduljabbar ɗin Lauyan da zai kareshi kamar yadda wakilin Freedom Radio Aminu Abdu Bakanoma ya rawaito.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!