Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zargin Maita: Uwa da Ɗa sun rantse da Al’ƙur’ani

Published

on

Kotun shari’ar Musulinci mai lamba daya dake nan Kano ta rantsar da wata uwa da ɗan ta da Alkur’ani mai girma saboda zarginsu da laifin  ɓatawa wata wata mata da cewa ita Mayyace.

Tun da fari Rukayya Kabiru ita ce aka batawa suna kuma ita ce ta shigar da  makotan ta kara kan zargin maita da suke mata.

Rabi’atu Idris da Ɗanta Muhammad Idris ne wadanda ake kara har ma shi dan yayi ikirarin zai kashe Rukayya bayan kiranta da mayya da suke yi.

A zaman kotun na yau mai shari’a Munzali Tanko ya tambayi wadanda ake kara su biyu kan zargin da akeyi musu inda suka musanta dukka zargin da ake musu.

A nan ne mai shari’a ya nemi mai kara da ta kawo shaidun da za su tabbatar da cewa sun bata mata suna sai dai tace bata da shaidu, inda anan ne mai shari’a ya rantsar da su da Alkur’ani mai girma kamar haka.

mai shari’a Munzali Tanko Soron Dinki ya yi musu nasiha mai ratsa zuciya tare da gargadinsu cewa kada su bari wata fitina ta kara faruwa a tsakaninsu a matsayinsu na maƙota.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!