Connect with us

Labarai

Ƙungiyar Gwamnonin Arewa ta bayyana kaɗuwa bisa rasuwar tsohon shugaban Ƙasa Buhari

Published

on

Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa NSGF ta bayyana kaɗuwa da alhininta game da rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, tana mai cewa wannan babban rashi ne ba wai ga Arewa kadai ba, har da kasa baki ɗaya.

 

Wannan na cikin sanarwar da Shugaban kungiyar kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya CON, ya fitar a ranar Lahadi.

 

A cewar Inuwa Yahaya, marigayin tsohon shugaban ƙasa Buhari mutum ne da rayuwarsa ta ƙunshi ladabi, rikon gaskiya da ƙwazo wajen hidima ga ƙasa tun daga lokacin da ya fara aiki a matsayin matashin soja, har zuwa shugabancinsa na mulkin soja da na dimokuraɗiyya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!