Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kadan ya rage mu kawo karshen matsalolin tsaro – Buhari

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci gwamnonin Arewa da su tattauna tare da kirkiro hanyoyin hadin gwiwa da jami’an tsaro da kuma jama’a, domin kawar da ta’addanci da matsalolin tsaro a yankunan.

Buhari ya bayyana haka ne a yau Alhamis 25 ga watan Fabrairu yayin taron kungiyar gwamnonin Arewa da aka gudanar a jihar Kaduna, ya kuma samu halartar shugabannin majalisar sarakunan arewacin kasar nan.

Shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin tarayya da ya wakilci shugaban kasa, Ibrahim Gambari, ya ce, gwamnatin tarayya za ta cigaba da magance ayyukan masu tada kayar baya da ‘yan fashi da masu satar mutane da kuma sauran masu laifi da ke zama barazana ga yan kasa nagari.

Haka kuma, Mai alfarma Sarkin Musulmai Muhammadu Sa’ad, ya ce, “Za mu cigaba da marawa gwamnonin baya, ina kuma jinjina ga gwamnonin na arewa da suka je wuraren da matsalolin tsaro suka faru don jajantawa tare da tsayawa don ganin mutanen arewa su samu karbuwa a wuraren.”

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!