Connect with us

Coronavirus

Ƙarin mutane 238 sun kamu da Korona jiya Lahadi inji NCDC

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce a jiya litinin ta yiwa mutane 238 gwajin cutar Corona cikin su kuma an gano karin mutane 12 da suka harbu da cutar.

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ce ta bayyana hakan a shafinta na twitter, inda ta ce a yanzu sauran mutane 213 ne suka rage masu jinyar cutar.

A kasa baki daya kuwa, cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta kasa NCDC ta ce a jiya Lahadi an sami karin mutane 521 cikin jihohi 20 na fadin kasar nan.

Hukumar ta ce da samun wannan kari ya zuwa yanzu cutar ta kama adadin mutane 152,074 cikin su kuma guda 128,619 sun warke sai kuma guda 1,839 da suka hallaka a dalilin cutar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!