Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƙungiyar Mata masu katin zabe ta goyi bayan hukuncin Kotun daukaka kara

Published

on

Kungiyar Mata masu katin Zabe na ƙasa reshen Kano ta ce tana goyon bayan hukuncin da kotu ta yanke kan zaben gwamnan Kano na zaɓen 2023 domin bayyana cikakken goyon bayan su da amincewar su ga hukuncin baya-bayan nan da kotun daukaka kara ta tabbatar dangane da zaben gwamna na 2023

Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a yayin taron manema labarai da ya gudana ƙarƙarshin jagoranci Hajiya Halima Tanko Rogo

Hukuncin da aka yankewa Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya cancanta wata shaida ce da ke nuna irin karfin da hukumomin dimokaradiyyar mu ke da shi da kuma bin doka da oda

A tsawon wannan lokaci mun jajirce wajen tabbatar da gaskiya, da mutunta tsarin doka da ke tafiyar da tsarin zaben mu

Binciken da kotun ta yi da kuma tabbatar da sakamakon zaben ya nuna sahihancin tsarin dimokuradiyya da kuma tabbatar da ra’ayin jama’a

Nasarar da Nasiru Yusuf Gawuna ya samu ba wai nasa ne kawai ba, a’a, nasara ce ta gamayya da muradun al’umma

A yayin da muke ci gaba, ya zama wajibi mu goyi bayan shawarar da aka amince da ita, mu yi watsi da duk wani bambance-bambancen da ke tsakaninmu, tare da hada kai wajen cimma burin ci gaban jiharmu

Ya kamata wannan hukunci ya zama wani ƙarfi don ƙarfafa ƙoƙarinmu na gina kyakkyawar makoma ga kowa

Muna kira ga masu ruwa da tsaki, ba tare da la’akari da siyasa ba, da su rungumi wannan sakamakon cikin alheri

Muna kira ga Abba Kabir Yusuf da tawagarsa, da nufin hada kai don samar da kyakkyawar makoma ga Kano

Muna fatan kyakkyawan shugabanci, da ci gaba ga al’ummar mu a karshe muna mika sakon taya murna ga Nasiru Yusuf Gawuna bisa tabbatar da shi a matsayin wanda ya cancanta ya lashe zaben gwamna a 2023

Allah ya sa wa’adin mulkinsa ya kasance mai cike da wadata, haɗa kai da ci gaba da zai amfanar kowanne al’umma na jihar kano

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!