Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƴan Chana ne suka kawo matsalar tsadar Kaya: MARTAN

Published

on

Hana ƴan chana shigowa kasuwanci a jihar Kano shine zai habbaka kasuwanci a jihar KanoG

Gamayyar kungiyoyin ƴan kasuwar ƙasar nan reshen jihar Kano ta ce hana ƴan ƙasar Sin Chana shigowa kasuwar kwari shi zai taimaka wajen samar da tsayayyen farashi a harkar kasuwancin su

Wannan jawabi ya fito daga bakin shugaban ƙungiyar reshen Kano Alhaji Auwal Illiyasu yayin da yake zantawa da manema labarai kan yadda ake samin ƙaruwar farashi a cikin kasuwar kwari

 

Auwal ya kuma ce yadda ƴan Sin suke shigowa cikin kasuwar kwari suna ganin yadda ƴan kasuwa suke shiyar da kaya ya sanya suma suke sake ƙara farashi wanda hakan ya sanya kullum idan sukaje saro kaya yakan ƙara tashi

Haka kuma sun samar da yara a cikin kasuwar ta kwari domin zuwa suna zagayawa domin jiyo musu yadda ƴan kasuwar suke shiyar da kayan da suka shiya daga hannun ƴan Chana

Sai ƴan kasuwar na kira ga gwamnati da ta dakatar da ƴan Sin Chana daga shigowa kasuwannin Kano wanda hakan zai daidaita farashin kaya a kasuwar

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!