Connect with us

Ƙetare

Ƴan ta’addan ISWAP sun kai hari sansanonin Soji a Kamaru

Published

on

Rahotanni daga Arewa maso Gabashin Najeriya, sun nuna cewa, ƴan ta’addan ISWAP sun kai hari sansanin soji a garuruwan Banki da Freetown da ke kusa da iyakar Kamaru, inda mutane sama da dubu biyar suka tsere zuwa cikin Kamaru.

 

Rahotonni sun bayyana cewa, maharan sun yi yunkurin mamaye sansanin sojojin ne cikin dare, sai dai bayan musayar wuta tare da samun dauki daga sojojin sama, aka fatattake su, inda sojoji biyu da fararen hula bityu suka rasa rayukansu tare da lalata gidaje da dama.

 

Harin ya biyo bayan farmakin da aka kai Darul Jamal makonni biyu da suka gabata, inda aka kashe mutane kusan 90.

Duk da raguwar tashin hankali tun bayan shekarun 2013 zuwa 2015, rikicin Boko Haram da ISWAP ya ci gaba da addabar arewa maso gabashin kasar nan, inda ya hallaka fiye da mutane 40,000 tare da tilasta sama da miliyan biyu barin gidajensu tun 2009.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!