Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƴancin kai: Najeriya na cikin jerin ƙasashen da aka bari a baya – Tanko Yakasai

Published

on

Wani tsohon dan siyasa anan Kano ya bayyana cewa har yanzu Najeriya na cikin jerin ƙasashen da aka bari a baya musamman ta fannin ci gaba.

Alhaji Tanko Yakasai ne ya bayyana hakan jim ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan Freedom Radiyo, wanda yayi duba kan bikin cika shekara 61 da samun yancin kan Najeriya.

Alhaji Tanko Yakasai ya ce, akwai kasashe da suka samu ƴanci tare da kasar nan amma a yanzu kasashen sun yiwa Najeriya fitinkau.

“Idan muka yi duba a ɓangaren ilimi za mu ga cewa tuni ɓangaren ya samu koma baya, ta yadda a yaznu mun gwammace mu tura yaran mu ƙasashen duniya don siyo karatu sama da mi inganta makarantun ƙasar ma” in ji Yakasai.

Alhaji Tanko ya kuma ce “Rungumar tsarin noma ita ce hanya ɗaya da za a magance matsalar tattalin arziƙi da kuma barazanar tsaron da ake fuskanat, domin kuwa duk wanda ya samu aikin yi ba zai sanya kan sa a mummunar ɗabi’a ba”.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!