Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NEMA ta karbi yan Nijeriya 146 da suka makale a Yamai

Published

on

Hukumar ba da Agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA ta karbi ‘yan kasar 146 da suka makale a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar, dake kan hanyarsu ta zuwa kasashen ketare da nufin neman arziki.

Shugaban hukumar shiyar Kano Dakta Nura Abdullahi ne ya bayyana haka a jiya Alhamis yayin zantawarsa da Freedom radiyo.

Dakta Abdullahi ya ce ‘wadanda aka kamo ‘yan asalin kasar sun dawo ne ta hanyar wani shiri na mayar da ‘yan gudun hijira gida, karkashin kulawar hukumar kula da ‘yan cirani ta duniya IOM’.

Wadanda aka dawo da su sun hada da maza 56, da mata 39, sai yara 51 da suka hadar a mata 35 da maza 16 daga jihohin Katsina, Kano, Adamawa, Lagos, Imo, Enugu, Edo, da dai sauransu.

Rahoton: Ahmad Kabo Idris

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!