Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gobara tayi sanadiyar mutuwar mutum uku, da konewar gidajen dubu a Barno

Published

on

Akalla wasu ‘yan gudun hijira uku ne suka mutu, sannan sama da gidaje 1000 suka kone bayan da gobara ta tashi a sansanin ‘yan gudun hijira a Muna da ke Maiduguri a jihar Barno.

Gobarar ta tashi ne da misalin karfe 6 na safiyar Laraba kuma ta dauki sama da awa daya kafin jami’an kashe gobara su shawo kan ta.

Babban Darakta Hukumar Ba da Agajin Gaggawa a Jihar Borno Dakta Barkindo Muhammad Sa’idu ne ya bayyana hakan a Maiduguri, inda ya ce kungiyar sa kai na CJTF, da jami’an tsaro da ma su kansu ‘yan gudun hijira, sun taimaka gaya wajen kashe gobarar.

 

Rahoton: Madeena Shehu Hausawa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!