Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano, ta buƙaci gwamnatin Injiniya Abba Kabir Yusuf, da ta gina titi a hanyar da ta tashi daga Unguwar Maidile Kwanar gidan Kaji ta bi ta unguwannin Shekar Mai ɗaki da Bubbugaji zuwa Gidan Mairodi duk a ƙaramar hukumar Kumbotso.

Majalisar ta buƙaci hakan ne a zamanta na yau Litinin sakamakon ƙudurin da mai tsawatarwar na zauren kuma Wakilin Kumbotso Mudassir Ibrahim Zawaciki ya gabatar.

Yayin gabatar da ƙudurin, ɗan majalisar na Kumbotso, ya buƙaci haɗin kan takwarorinsa na majalisar wajen yin kira da murya ɗaya ga gwamnatin wajen gudanar da aikin hanyar.

Da yake goyon bayan ƙudurin dan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Gabasawa Zakariyya Abdullahi Nuhu, bayyana alfanun samar da irin waɗannan hanyoyi ya yi ta na mai cewa ya kamata gwamnatin ta gaggauta gina su.

A dai zaman na yau, ƙudurin dokar kafa cibiyar yaƙi da sha da cutuka masu yaɗuwa, da gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf, gabatar wa majalisar dokokin, ya tsallake karatu na ɗaya a zauren.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!