Labarai
Dole ƴan Najeriya sun samu tsaro ta kowane hali Babban Hafsa

Babban hafsan tsaron Najeriya Janar Olufemi Oluyede ya buƙaci dakarun tsaro su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ƴanbindiga a jihohin arewa maso yamma, inda ya nanata cewa dole a tabbatar da ƴan Najeriya sun samu tsaro ta kowane hali.
Janar Oluyede ya bayyana haka a ziyarar da ya kai wa sojojin da suke aiki na musamman na watau Operation Fansan Yamma a garin Gusau da ke jihar Zamfara.
Hafsan ya bayyana shirin rundunar tsaron Najeriya na kawo ƙarshen matsalolin ƴanbindiga a jihohin arewa ta yamma, inda ya ƙara da cewa idan aka cigaba da matsa wa ƴanbindigar lamba ne za a samu sauƙi da zaman lafiyar da ake buƙata.
You must be logged in to post a comment Login