Labarai
kotu ta bada umarnin tsare shugaban jam’iyyar ADC

Wata kotun majistare da ke Birnin Kebbi, ta bayar da umarnin a tsare shugaban wani ɓangare na jam’iyyar ADC, Sufyanu Bala, bisa zarginsa da raina umarnin kotu kan takaddamar shugabancin jamiyyar.
Kotun ta ce za a ci gaba da tsare shi har zuwa lokacin sauraron bukatarsa ta neman beli.
Lauyan masu ƙara ya bayyana cewa matakin ya zama dole domin tabbatar da mutunta doka, ya na mai zargin Sufyanu Bala, da karya umarnin kotu.
Sai dai lauyan wanda ake ƙara ya musanta hurumin kotun majistare ɗin kan shari’ar, ya na cewa batun ya na gaban babbar kotu.
A nasa ɓangaren, Sufyanu Bala, ya zargi gwamnatin jihar da hannu a rikicin domin kawo cikas ga jam’iyyar.
Rikicin ya daɗe ya na faruwa a jam’iyyar ADC a Kebbi, inda ɓangarori daban-daban ke ikirarin shugabanci, lamarin da ke jefa shakku kan haɗin kan jam’iyyar gabanin zaɓukan shkarkar 2027.
You must be logged in to post a comment Login