Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Walter Onnoghen:ya kalubalanci rashin cancantar alkalin kotun da’ar ma’aikata

Published

on

Dakataccen babban jojin Najeriya Walter Onnoghen ya kalubalantar rashin cancantar alkalin kotun da’ar ma’aikata Danladi Umar wajen cigaba da shari’ar, da ake masa kan zargin bayyana kadarorin da ya mallaka

A jiya ne lauyoyin da suke kare Walter Onnoghen suka nemi  Danladi Umar  da ya janye daga cigaba da gabatar da karara a matsayin sa na alkalin kotun da’ar ma’aikata saboda zargin karbar na goro na Naira miliyan 10 da hukumar EFCC ke yi.

Karar mai dauke da sa hannun Chris Uche mai darajar SAN da Chief Sebastine Hon mai darajar SAN da Okon Efut da Chief Ogwu Onoja mai darajar SAN da Noah Abdul da George Ibrahim.

Lauyoyin sun nemi Daladi Umar da ya janye daga cigaba da gabatar da karar saboda rashin cancatar sa

Dakataccen baban jojin kasar ya bayyana Danladi Umar da cewa bashi da aniyya mai kyau, kuma shi ne mai gabatar da karar kuma shi ne alkali a gefe guda kuma shine mai kare wanda ake gabatar da kara.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!