Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kotun daukaka kara ta soke karar da Onnoghen ya shigar gabanta

Published

on

Kotun daukaka kara dake Abuja ta soke daukaka karar da dakataccen babban jujin kasar nan Walter Onnoghen ya shigar gaban ta.

Kotun ta ce karar an rigaya an saurare ta a kotun da’ar ma’aikata kuma tuni ma da aka kammala sauraran ta a kotun.

A yayin da ake yin shari’ar karkashin jagorancin mai shari’a Stephen Adah, kotun daukaka kara ta ce umarnin gaggawa da kotun da’ar ma’aikata ta bayar ya saba wa damar da dakataccen babban jujin kasar nan yake da shi nayi masa adalci yayin sauraran da yanke hukuncin karar.

Kotun daukaka karar ta bayyana cewa babu bukatar dakataccen babban jojin Najeriya ya kalubalanci umarnin gaggawar da kotun da’ar ma’aikata ta bayar na cewa babban jujin kasar nan Walter Onnoghen ya sauka daga kan mukamin sa.

Dalilin haka ne kotun ta yi watsi da daukaka karar da babban jujin ya yi sakamakon umarnin da shugaban kotun da’ar ma’aikata, mai shara’a Danladi Umar ya baiwa Walter Onnoghen da ya sauka daga kan mukamin sa na babban jujin kasa har sai an kammala shari’ar da ake masa na kin bayyana wasu daga cikin kadarorin da ya mallaka

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!