Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sanata Ahmad Lawan ya musanta zargin jagorantar gyara ga kundin tsarin mulkin kasa

Published

on

 

‘Yan majalisar dattawa da ke goyon bayan shugaban masu rinjaye na majalisar Sanata Ahmed Lawan sun musanta cewa, Sanata Ahmed Lawan idan ya samu nasarar zama shugaban majalisar zai jagoranci gyara ga kundin tsarin mulkin kasar nan don bai wa shugaban kasa Muhammadu Buhari zarcewa karo na uku.

Mai magana da yawun kungiyar Sanata Aliyu Sabi Abdullahi ne ya bayyana haka ta cikin wata sanarwa da ya fitar jiya a Abuja.

 

Sanarwar ta ce ya zama wajibi su mayar da martani kan labaran da aka yada cewa Sanata Ahmed Lawan zai jagoranci yin gyara ga kundin tsarin mulkin kasar nan don baiwa shugaban kasa Muhammadu Buhari damar zarcewa karo na uku, idan wa’adin mulkin sa ya kare.

 

A cewar sa wasu ‘yan siyasa ne kawai da ke da burin jagorantar majalisar suka kitsa maganar da nufin zubar da kimar Sanata Ahmed Lawan.

 

Sanata Aliyu Sabi Abdullahi ya kuma ce lokacin da Sanatoci ‘yan jam’iyyar APC suka gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kwanaki uku da suka gabata, ya shaida musu cewa ya tsaya takarar shugaban kasa har sau biyar kuma wannan shine na karshen da yayi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!